1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka: Hukuncin kotu kan dokar baki

Abdul-raheem Hassan
February 10, 2017

Wata kotun daukaka kara ta Amirka da ke San Francisco ta yi watsi da bukatar shugaba Donald Trump da ke neman gwamnatinsa haramtawa wasu kasashen musulmi bakwai shiga kasar.

https://p.dw.com/p/2XIuo
USA Präsident Donald Trump
Hoto: picture-alliance/abaca/O. Olivier

A wani zama da ta yi, kotun mai alkalai uku ta ce bangaren Trump bai gabatar da wata hujja mai gamsarwa ba da zai sa a cigaba da aiwatar da wannan doka ta hana baki daga kasashen Somalia da Yemen da Syria da Iran da Iraqi da Sudan da kuma Libya shiga kasar ta Amirka ba. Kotun ta yi nuni da cewa akwai bukatar al'ummar Amirka su mutunta dokar kasa ciki har da shugaba, to sai dai tuni Shugaba Trump ya wallafa a shafin sa na Twitter cewa akwai kotu na gaba wanda hakan ke nuni da cewar zai daukaka kara inda a share guda ya ce wajibi a dau matakan tsare kasa.