1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka: Sabon babin dangantaka da Turkiyya

Ramatu Garba Baba
December 28, 2017

Amirka ta sanar a wannan Alhamis cewa za ta sake bude ofishin huldar jakadancinta da ke Ankara babban birnin kasar Turkiyya bisa abin da ta kira wanzuwar zaman lafiya da ingantar tsaro da aka samu a kasar.

https://p.dw.com/p/2q491
Ukraine Botschaft der USA in Kiew
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Dolzhenko

Matakin na nufin kasashen biyu za su ci gaba da yin hulda kamar yadda suka saba a baya dama bayar da takardar izinin shiga kasashen juna a kasar da ta sha fama da ayyukan kungiyar IS da kuma rikicin cikin gida da ya biyo bayan yunkurin juyin mulki. An sami sa-in-sa da ya kai ga tsamin dangantaka bayan da hukumomin Turkiyyan suka kama tare da tsare wani jami'in a ofishin jakadancin kasar Amirka a watan Oktoba. Tuni dai Turkiyya ta baiyana farin ciki kan sanarwar Amirka.