1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka ta dauki mataki kan wasu jami'an Burundi

Gazali Abdou TasawaNovember 24, 2015

Shugaba Barack Obama ya haramta balaguro da kuma taba kudaden ajiyan banki ga wasu jami'an kasar Burundi hudu da ake zargi da haddasa rigingimu da kasar ke fama da su.

https://p.dw.com/p/1HB3E
Burundi Adolphe Nshimirimana Sarg Beisetzung Trauerfeier
Hoto: picture-alliance/AP Photo/Berthier Mugiraneza

Mutanen da matakin ya shafa sun hada da wasu na kusa da Shugaba Nkurunziza wato Alain-Guillaume Bunyoni, ministan tsaron kasar ta Burundi da kuma Godefroid Bizimana, mataimakin babban daraktan hukumar 'yan sandan kasar da kuma wasu biyu na bangaren adawa da suka hada da Janar Godefroid Niyombare wanda ya jagoranci juyin milkin da bai yi nasara ba, sai kuma Cyrille Ndayirukiye tsohon ministan tsaron kasar.

Wannan mataki na Shugaba Obama ya biyo bayan wani mai kama da irinsa da Kungiyar EU ta dauka a farkon watan Oktoban da ya gabata, kan wasu jami'an kasar ta Burundi.