1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka za ta dauki mataki kan Koriya ta Arewa

Gazali Abdou Tasawa
August 29, 2017

Jakadar Amirka a MDD Nikki Haley ce ta Amirka za ta dauki wani kwakkwaran mataki na musamman kan Koriya ta Arewa biyo bayan sabon gwajin makami mai lizzami da ta yi a wannan Talata.

https://p.dw.com/p/2j3AO
UN-Sicherheitsrat- US-Botschafterin Nikki Haley
Hoto: picture-alliance/EuropaNewswire/L. Rampelotto

Amirka ta sanar da shirin daukar wani kwakkwaran mataki na musamman kan Koriya ta Arewa biyo bayan sabon gwajin makami mai lizzami da ta yi a wannan Talata da ya bi ta sarararin samaniyar kasar Japan. Jakadar Amirka a MDD Nikki Haley ce ta sanar da hakan a daidai lokacin da kwamitin sulhu na MDD  ke shirin gudanar da wani taron gaggawa a wannan Talata domin nazarin barazanar nukiliyar Koriya ta Arewa.