1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka za ta kara sanyawa Iran takunkumi

Ahmed Salisu
June 22, 2019

Shugaban Amirka Donald ya bayyana cewar gwamnatinsa za ta kara kakabawa Iran karin takunkumi biyo bayan harbo jirginta maras matuki da ta yi a 'yan kwanakin da suka gabata.

https://p.dw.com/p/3KvFg
USA | Donald Trump
Hoto: picture-alliance/dpa/abaca/Pool/Polaris/M. Theiler

Shugaban Amirka Donald ya bayyana cewar gwamnatinsa za ta kara kakabawa Iran karin takunkumi biyo bayan harbo jirginta maras matuki da ta yi a 'yan kwanakin da suka gabata.

Shugaban ya ambata hakan ne dazu gabannin fara tattauna da masu bashi shawara. Ko da dai bai yi karin haske kan irin takunkumin da Amirka din za ta kara kakabawa Iran din ba amma dai ya ce takunkuman suna da yawan gaske. Wannan dai na zuwa ne dadai lokacin da kasashen duniya ke cigaba da kira ga Tehran da Washington kan su yi amfani da hanyoyi na diflomasiyya wajen warware takaddamar da ke akwai tsakaninsu.