1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An ba da sakamakon zaben shugaban kasar Mai

August 2, 2013

Hukumar zaben kasar Mali ta ba da sanarwar cewa tsohon firaministan kasar, Ibrahim Boubacar Keita ya lashe zaben shugaban kasar, zagayen farko, amma ba da gagarumin rinjaye ba.

https://p.dw.com/p/19J52
Artikel: Mali geht in die Stichwahl für den 2. August 2013 Kater-Stimmung bei den Unterstützern von Ibrahim Boubacar Keita Titel: DW_IBK1 Schlagworte: Ibrahim Boubacar Keita, Präsidentschaftskandidat, Mali, Stichwahl Wer hat das Bild gemacht/Fotograf?: Katrin Gänsler Wann wurde das Bild gemacht?: 2. August 2013 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Bamako, Mali
Hoto: DW/K.Gänsler

 Hukumar ta  ce a don haka ya zamo wajibi a gudanar da zaben zagaye na biyu a ranar11 ga wannan wata na Agusta tsakanin shi Keitan da tsohon minisan kudin kasar,  Soumaila Cisse da ya yi na biyu. Ga dai yadda Kanal Musa Sinko Koulibali, ministan cikin gidan kasar ta Mali ya ba da sanarwar sakamakon zaben.

  Ya ce: "Soumaila Cisse ya samu kuri'u  dari shida da dari tara da daya wato kashi 19 da digo 44 daga cikin dari. Ibrahim Boubacar Keita shi kuma ya samu kuri'u miliyan guda da dubu 22 da dari shida da 57 wato kashi 39 da digo 24 daga cikin dari."

Shi dai zaben shugaban kasar ta Mali na zaman wani  mataki na maido da kwanciyar hankali da mulkin demokradiya a wannan kasa. Watanni shida ne dai sojojin Faransa suka kwashe suna aiki a kasar domin murkushe 'yan kishin Islama da ke arewacin kasar.  Gabanin hakan ne kuma aka hambarar da Shugaba Amadou Toumani Toure.

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Yahouza Sadissou Madobi