1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bude taron kolin EU kan samar da aikin yi

October 24, 2013

Shugabannin tarayyar Turai da ke taron kolin yini biyu a birnin Brussles za su duba hanyoyin magance matsalar yawan marasa aikin yi a cikin kasashen kungiyar.

https://p.dw.com/p/1A5oZ
Germany's Chancellor Angela Merkel (L) talks with France's President Francois Hollande (R) at a European Union leaders summit in Brussels October 24, 2013. German and French accusations that the United States has run spying operations in their countries, including possibly bugging Chancellor Angela Merkel's mobile phone, are likely to dominate a meeting of EU leaders starting on Thursday. The two-day Brussels summit, called to tackle a range of social and economic issues, will now be overshadowed by debate on how to respond to the alleged espionage by Washington against two of its closest European Union allies. REUTERS/Yves Herman (BELGIUM - Tags: POLITICS)
Hoto: Reuters

Shugabannin kasashen kungiyar tarayyar Turai sun bude taron kolinsu na yini biyu wanda cece-kuce game da leken asirin da ake zargin Amirka ta yi wa shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ya mamaye shi. Tuni dai shugannin EU suka nemi sanin gaskiyar lamarin daga gwamnatin Amirka. A gun taron shugabannin na tarayyar Turai za su kuma tattauna game da matsalar yawan marasa aikin yi da ta yi wa musamman matasan nahiyar katutu. Alkalumma sun yi nuni da cewa tarayyar EU dake zama wata kungiyar cinikaiya mafi girma a duniya, yawan marasa aikin yi a tsakanin matasa 'yan kasa da shekaru 25 da haihuwa ya kai kashi 23.3 cikin 100. Ko da yake shugabannin za su yi tattaunawa mai tsawo a kan wannan matsala amma ba wanda ya hango mafita daga matsalar ba saboda basussukan dake kan kasashen kungiyar.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu