1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana cigaba da zanga-zanga sakamkon kisan kai a Amirka

Zulaiha Abubakar
May 29, 2020

Shugabar hukumar kare hakkin bil Adama ta Majalisar Dinkin Duniya Michelle Bachelet ta bukaci gwamnatin Amirka ta haramtawa 'yan sanda kashe 'yan kasar bakar fata.

https://p.dw.com/p/3cwRI
USA Minneapolis | Tod George Floyd nach Polizeigewalt | Ausschreitungen & Protest
Hoto: Reuters/C. Barria

Wannan kira ya biyo bayan barkewar zanga-zanga a Minneapolis, sakamakon mutuwar wani bakar fata mai suna George Floyd bayan shakewar da wani 'dan sanda farar fata ya yi masa. Bachelet ta kuma kara da bayyana wannan mummunan al'amari a matsayin guda cikin adadin Amirkawa bakar fata da suka rasa rayukansu a hannun jami'an tsaro ko kuma al'ummar kasar ta Amirka farar fata.

Michelle Bachelet wacce ta kasance tsohuwar shugabar kasar Chile ta jaddada muhimmancin sauya hanyoyin da 'yan sanda ke amfani da su wajen cafke masu laifi bayan ta bukaci a dinga gurfanar da jami'an tsaron da suka wuce makadi da rawa yayin gudanar da aiki. Hukumar kare hakkin dan Adam din ta Majalisar Dinkin Duniya ta ja hankalin masu zanga-zangar su guji tarzomar da za ta haifar da asarar dukiyoyi.