1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An cika shekaru biyu da fara kaɗawar guguwar neman sauyi a Tunisiya

December 17, 2012

A garin Sidi Bouzid an jefi shugaban ƙasar Tunisiya wurin bikin tuni da zagayowar fara zanga-zangar neman 'yanci.

https://p.dw.com/p/174FN
Tunisia's President Moncef Marzouki waits prior his statement during the 101st International Labor Organization, ILO, Conference at the European headquarters of the United Nations in Geneva, Switzerland, Friday, June 8, 2012. (Foto:Keystone/Martial Trezzini/AP/dapd).
Moncef Marzouki shugaban TunisiyaHoto: AP

A wannan Litinin, al'umar Tunisiya suka fara bikin cikar shekaru biyu da ɓarkewar zanga-zangar juyin-juya hali, wadda ta kifar da mulkin shugaba Zin El-Abedine ben Ali, sannan ta bazu zuwa sauran ƙasashen larabawa.

Shugaban ƙasa Moncef Marzouƙi da shugaban Majalisar Dokoki Mustapha Ben Jaafar, sun halarci garin Sidi Bouzid, dake matsayin cibiyar zanga-zangar, to saidai duban mutane sun tarbe su da ihu da jifa da duwatsu,tare da zargin su da cin amanar juyin-juya hali.

Mohamed Ali shine shugaban ƙungiyar gwagwarmayar ci gaban Sidi Bouzid ya yi huruci ya na cewa:

" Ba su yi komai ba,illa neman kuɗi su cika alhifansu.

Sam! ba su damu da halin da talaka ke ciki ba.Su da kansu sun yi imanin cewar basu tsinana wani abin azo a gani ba, a cikin wannan shekaru biyu".

Dubun-dubatar mutanen da suka hallara a dandalin ƙwatar 'yanci, sun yi ta rera kalamomi masu buƙatar shugabanin su yi murabus.

Jama'a da dama a ƙasar Tunisiya na zargi magabatan da kasa tabura komai, domin magance manyan ƙalubale da ƙasa ke fama da su, hasali ma rashin aiki yin da talauci.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Usman Shehu Usman