Hukumar zaben malawi ta jinkirta fidda sakamako
May 26, 2019Lazarus Chakwera, na Malawi Congress Party (MCP) ya fada wa kotun cewa sun gano kura-krai a gundumpomi 10 cikin gundumomi 28, inda aka yi aringizon kuri'u lokacin kada kuri'a, bisa yin amfani da tawada da kuma birkita takardun zabe. Don haka babban kotun kasar ya umarci a dakatar da bada sakamakon zaben, har sai an sake kirga wasu gundomomi da ake da shakku a kansu. Babbar daraktar hukumar zaben kasar Jane Ansah, ta bayyana cewa a yanzu ba za ta ci gaba da sanar da sakamako ba, har sai an kammala ka'idojin shari'a. A bisa dokokin kasar Malawi, duk wasu korofe-korofen zabe sai an kammala su, kana a sanar da sakamakon zaben a tsukin kwanaki takwas bayan zabe. Tuni dai bore ya barke daga bangaren 'yan adawa, inda a Lilongwe babban birnin kasar, masu boren suka yi ta yaga postocin jam'iyya mai mulki, kana suka yi ta fasa gine-ginen gwamnati. An dai baza jami'an 'yan sanda don shawo kan lamarin. Shugaba Peter Mutharika na neman wa'adi na biyu amma yana fiskantar mummunar adawa.