1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An fara kaɗa ƙuri'a a zagaye na biyu na Zaɓen Mali

August 11, 2013

Tsohon Firaminista Ibrahim Boubacar Keita na RPM, da Soumaila Cisse na URD, sune ke fafatawa a zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasar

https://p.dw.com/p/19NZP
Symbolbilder/2013_08_09_praesidentschaftswahlen-mali.psd

Sama da mutane miliyan shida ne waɗanda suka cancanci yin zaɓen ke kaɗa ƙuri'a a zaɓen wanda ke cike da mahimmanci ga ƙasar da ta yi fama da rikicin siyasa da kuma yaƙi bayan juyin mulki da sojoji suka yi a shekarun 2011.

Manyan ƙalubale da ke a gaban duk wanda za a zaɓa,sune yaƙi da cin hanci da karɓar rashawa, da rashin tsaro a yankin arewacin ƙasar da kuma zaman kashe wonda na jama'a galibi matasa. Souleimane Drabo shi ne editan wata mujalla ta ƙasar da ake kira da sunnan Essor.

Ya ce : ''Abin da ake jira kana kuma ake tsamani shi ne mutumin da za a zaɓa ya kasance ya samu cikakkiyar dama ta gudanar da shugabanci fiye da wanda shugabannin da suka shuɗe suka samu''. A zagaye na farko dai na zaɓen Ibrahim Boubacar Keita ya samu kishi 40 cikin ɗari na ƙuri'un da aka kaɗa yayinda Soumaila Cisse ke da ƙasa ga kishi 20.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Yahouza Sadissou Madobi