1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An fara sauraron kalubalantar zaben shugaban Kenya

March 27, 2013

A wannan Laraba kotun kolin kasar Kenya ke sauraron mahawara kan kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar

https://p.dw.com/p/184kZ
Riot policemen seated in a truck pursue supporters of the Coalition for Reforms and Democracy (CORD) outside the Supreme Court compound in the capital Nairobi, March 16, 2013. Kenya's defeated presidential contender Raila Odinga filed a legal challenge to his election loss on Saturday in a major test of the country's democratic system five years after a disputed vote triggered deadly tribal clashes. REUTERS/Noor Khamis (KENYA - Tags: ELECTIONS POLITICS CRIME LAW CIVIL UNREST)
Hoto: Reuters

A wannan Laraba kotun kolin kasar Kenya ke sauraron kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar, wanda Uhuru Kenyatta ya lashe cikin wannan wata na Maris, shari'ar da ke zama zakaran kwaji na demokaradiyyar kasar.

Firaminista Raila Odinga wanda ya zo na biyu, a zaben na ranar 4 ga wata ke kalubalantar sahihancin sakamakon zaben. Ranar Asabar wa'adin ke cika ga kotun na ta yanke hukunci kan matsayin sakamakon zaben shugaban kasar ta Kenya.

Rikicin da ya biyo bayan sakamakon zaben shugaban kasa na shekara ta 2007, ya janyo mutuwan fiye da mutane 1200.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Zainab Mohammed Abubakar