1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An fara taron duniya kan sauyin yanayi

Lateefa Mustapha Ja'afarNovember 30, 2015

Kasashen duniya sun bude taron sauyi ko kuma dumamar yanayi da ake wa lakabi da Cop 21 a birnin Paris na kasar Faransa cikin yanayin tsauraran matakan tsaro.

https://p.dw.com/p/1HEUY
Masu zanga-zangar adawa da dumamar yanayi a yayin taron Paris
Masu zanga-zangar adawa da dumamar yanayi a yayin taron ParisHoto: Getty Images/AFP/M. Medina

Shugabannin kasashen duniya 150 sun hallara domin halartar taron ciki har da Shugaba Barack Obama na Amirka da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da na China Xi Jinping sai kuma shugaban kasar Rasha Vladimir Putin.

A yayin taron na makonni biyu ana sa ran shugabannin kasashen duniya za su amince da rage dumamar yanyi zuwa digiri biyu a ma'aunin Celsius. Taron dai za a gudanar da shi cikin tsauraran matakan tsaro biyo bayan harin ta'addanci da birnin na Paris ya fuskanta makonni biyun da suka gabata inda mutane 130 suka hallaka.

Masu rajin kare muhalli dai na gudanar da zanga-zanga a fadin duniya dangane da zargin kasashen da kin daukar matakan da suka dace domin kare muhalli, inda a Berlin babban birnin kasar Jamus a kalla mutane 10,000 ke yin zanga-zangar.