1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An gwabza faɗa tsakanin sojojin Mali da na MNLA

November 8, 2013

An ba da rahoton cewar an yi musanyar wuta ta bindigogi tsakanin sojojin Mali da dakarun ƙungiyar 'yan tawaye na MNLA a kusa da garin Menaka da ke a yankin arewaci na ƙasar.

https://p.dw.com/p/1AERq
Soldaten der Armee Malis üben am 07.05.2013 in Koulikoro, in Mali. Die EU-Ausbildungsmission (EUTM) läuft seit Anfang April. Die erste Gruppe von insgesamt 650 Soldaten hat nun die Grundausbildung begonnen. Aus Deutschland kümmern sich 17 Ausbilder um die künftigen Pioniere. Foto: Maurizio Gambarini/dpa
Hoto: picture-alliance/dpa

Wasu majiyoyin soji sun ce an kashe dakarun ƙungiyar 'yan tawaye na Abzinawa su guda uku kana aka cafke wasu, yayin da ɗaya sojin gwamnati ya jikkata. Faɗan ya faru ne a sailin da wasu mutane ɗauke da makamai a yankin da ke kan iyaka da Jamhuriyar Nijar suka yi wa sojojin gwamnatin Mali kwanton ɓauna waɗanda ke yin sintiri.

Kuma faɗan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Ban Ki Moon ya kammala wata ziyarar aiki a ƙasar.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh