1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gbagbo zai ci gaba da zama a gidan yari

Ramatu Garba Baba
January 18, 2019

Za a ci gaba da tsare Shugaban Kasar Cote d' Ivoire Laurent Gbagbo da Charles Blé Goudé tsohon shugaban kungiyar matasa na Patriote wanda kotun kasa da kasa ta ICC ta wanke a makon da ya gabata.

https://p.dw.com/p/3Bmbj
Internationaler Strafgerichtshof Den Haag Laurent Gbagbo
Hoto: picture-alliance/AP Photo/P, Dejong

Kotun ICC ta wanke Gbagbo da  Charles Blé Goudé a ranar Talata da ta gabata, amma yanzu za su ci gaba da kasancewa  a gidan kurku har zuwa daya ga watan Faibreru, bayan da alkalin alkalai na kotun ICC ya daukaka kara.Gbagbo wanda ake tsare da shi kusan shekaru bakwai a birnin Hague, an yi masa sharia'a ne kan laifuka na take hakkin dan Adama a tarzomar da ta biyo bayan zaben kasar na shekarun 2010 zuwa 2011 inda mutum sama da dubu uku suka rasa rayukansu.