An kai hari a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
May 29, 2014Talla
Lamarin ya auku a sakamakon wani hari na ramuwar gayya da wasu mutane ɗauke da makamai suka kai a kan wata Coci da ke a Bangui babban birnin jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.
Cocin wacce ake kira da sunan ''Notre dame de Fatima'' na tsakiyar birnin kusa da unguwar musulmi. Masu aiko da rahotannin sun ce an gwabza faɗa tsakanin sojin sa kai Kirista 'yan Ƙungiyar Antibalka da musulmi a Cocin inda dubban jama'a suka samu mafuka.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru aliyu