1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hari a Jihar Adamawa-Najeriya

Abdourahamane HassaneMay 19, 2015

Mutane aƙalla guda tara suka mutu kana wasu da dama suka jikkata a harin da aka kai a cikin wata kasuwa a Garkiɗa.

https://p.dw.com/p/1FSrD
Symbolbild Gewalt in Nigeria
Hoto: AMINU ABUBAKAR/AFP/Getty Images

Masu aiko da rahotannin sun ce mutumin da ya kai harin cikin kasuwar sayar da shanu ta garin na Garkiɗa.Tun farko jami'an tsaro sun gano yana ɗauke da bam, kuma a lokacin da suka bi shi da gudu ya sheƙa cikin kasuwar ya tayar da bam ɗin.

Wakilin DW a Yola ya ce yanzu haka hukumomin jihar na ƙoƙarin tantance,addadin mutane da lamarin ya rutsa da su.