1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai harin bam a Gombe daf da yaƙin neman zaɓe na PDP

Abdourahamane HassaneFebruary 2, 2015

Mutane aƙalla guda uku suka mutu yayin da wasu 18 suka jikkata.

https://p.dw.com/p/1EUhd
Anschlag in Gombe, NIgeria 02.02.2015
Hoto: Reuters/Afolabi Sotunde

An ba da rahoton cewar wani bam ya fashe a cikin wani wurin ajiye motoci da ke kusa da filin ƙwallon ƙafa na garin Gombe da ke a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Masu aiko da rahotannin sun ce bam ɗin ya fashe,mintocin uku bayan da ayarin motocin shugaban ƙasar Goodluck Jonathan ya ficce daga wani gangamin yaƙin neman zaɓe a filin ƙwallon wanda jam'iyyarsa da ke yin mulki wato PDP ta shirya.