1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai sabbin hare-hare a ƙasar Masar

Englisch-redJuly 20, 2014

Hukumomin tsaro sun ce wasu mutane ɗauke da makamai sun kai hari a kan wani wurin binciken da ke kan iyaka da Libiya.

https://p.dw.com/p/1Cfh5
Ägypten Anschlag Kairo 02.05.2014
Hoto: picture-alliance/dpa

Harin wanda aka kai a Wadi al Gadid da ke kan iyaka tsakanin Sudan da Libiya da kuma Masar ya yi sanadiyyar mutuwar sojoji 21 kana wasu huɗu suka jikkata. Hukumomin sun ce masu fautaucin miagun ƙwayoyi ne suka kai shi

To amma a cikin wata sanarwa da ya bayyana wani kakakin rundunar sojojin ƙasar, ya ce masu gwagwarmaya ke da alhaki. Sannan kuma ya ƙara da cewar maharan sun jefa wata roka a kan wani rubun ajiyar makamai wanda ya fashe. Wannan shi ne hari irinsa na biyu da aka kai a kan wannan cibiya a cikin wata guda.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman