1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Indiya ta kare kan ta kan kabilar Rohingya

Zulaiha Abubakar
January 3, 2019

Kasar Indiya ta mayar da rukuni na biyu na kabilar Rohingya gida bayan kaddamar da dokar kamen wadanda suka shiga Indiyan ta barauniyar hanya.

https://p.dw.com/p/3B0pK
Indien Grenze bei Moreh Rohingya-Männer vor Abschiebung nach Myanmar
Hoto: Reuters

Kabilar Rohingyan da jami'an tsaron Indiya suka mika wa hukumomin Kasar Myanmar sun hada da mata da maza wadanda suke tsare a Indiya tun shekara ta 2014 bayan samunsu da laifin kutsawa cikin kasar ta barauniyar hanya,kafin wannan lokaci dai hukumomin Indiya sun mayar da rukunin farko na Rohingya  a watan Oktober shekarar bara, Kabilar ta Rohingya da yawansu ya kai kusan dubu 700 sun tsinci kai a tsaka mai wuya tun daga lokacin da suka tserewa kisan da Sojojin kasarsu ke yi musu.