1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An nemi a daina nuna kyama ga masu Ebola

Ahmed SalisuOctober 27, 2014

Jakadiyar Amirka da ke zauren Majalisar Dinkin Duniya Samantha Power ta ce lokaci ya yi da za a daina nuna kyama ga masu dauke da Ebola.

https://p.dw.com/p/1Dckm
Ebola Patient in Monrovia Liberia
Hoto: Getty Images

Ms. Power ta kuma ce Amirka da sauran kasashen Duniya za su yi bakin kokarinsu wajen ganin an kawar da yaduwar cutar wadda yanzu haka ta hallaka mutanen da suka kai kusan dubu biyar yayin da wasu kimanin dubu goma ke dauke da ita.

Jakadiyar dai na wadannan kalamai ne yayin ziyararta a Gini, inda nan gaba kuma za ta isa Liberiya da Saliyo inda nan ma cutar ta yi ta'adin gaske da nufin ganewa idonta halin da ake ciki don sanin irin karin matakan da za dauka.

A wani labarin makamancin wannan, jami'an kiwon lafiya a Amirka sun ce suna sanya idanu kan wani karamin yaro da ya isa kasar daga Gini a karshen makon wanda yanzu haka ya ke fama da zazzafan zazzabi da kuma amai, wanda dukanninsu alamu ne na kamuwa da Ebola. To sai dai jami'an kiwon lafiya sun ce ya zuwa yanzu ba su kai ga tantacewa ko ya na dauke da cutar ba.