1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kiir zai ci-gaba rike madafan ikon Sudan ta Kudu

Zainab Mohammed AbubakarJuly 8, 2015

Matakin ya biyo bayan dage zaben kasar ne da majalisa ta yi saboda yakin batsatsa da ci-gaban zubar da jini da kasar ke ciki musamman a yankin arewaci.

https://p.dw.com/p/1Fv7j
Bildkombo Südsudan Riek Machar und Salva Kiir
Hoto: Getty Images/Zacharias Abubeker/Ashraf Shazly/Montage

An rantsar da Salva Kiir a matsayin shugaban Sudan ta Kudu na karin shekaru uku nan gaba. Majalisar dai ta zartar da cewar, Kiir baya bukatar a rantsar da shi a hukumance, kasancewar ya na kan karagar mulki.

Shugaban kasar ya yiwa majalisar alkawarin cewar, zai tattabar da zaman lafiya tare da sasantawa da shugaban tawaye Riek Machar. Fadan neman madafan iko na sojojin bangarorin biyu na tsawon watanni 18 dai, ya yi sanadiyyar dubban rayukan mutane.

A watan Maris da ya gabata ne majalisar dokokin Sudan ta kudu ta sanar da dage gudanar da zaben kasar, wanda ya kamata a gudanar a farkon watan Yuli da muke ciki, tare da kara wa'adin shugaba Kiir, mutumin da ya jagoranci wannan 'yar jaririyar kasar Afirka mai albarkatun man petur, tun samun 'yancinta daga Sudan shekara ta 2011. Sai dai a daya hannun tsohon mataimakinsa Machar, ya zargi Kiir da fadada wa'adin mulkinsa ba bisa ka'ida ba , tare da kalubalantarsa da ya sauka daga mulki.

An rantsar da Salva Kiir ne yini guda kafin bukin cikar kasar shekaru hudu da samun 'yancin kai. Bukukuwan da za su gudana a daidai lokacin da ake cigaba da gwabza fada a yankin arecin kasar mai albarkatun man petur.