1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sace ma'aikatan Red Cross a Afghanistan

August 16, 2014

An ba da rahoton cewar wasu 'yan bindigar sun sace wasu ma'aikatan ƙuingiyar su guda biyar a garin Herat da ke a gabashin ƙasar.

https://p.dw.com/p/1Cvrc
Kiew Proteste 18.02.2014
Hoto: Sergei Supinsky/AFP/Getty Images

Ƙungiyar ta Red Cross ta ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da ta gabata a sa'ilin da tawagar ma'aikatan ke kan hanyarta ta zuwa garin Herat a cikin mota.

A jiya jumma'a ma kafofin yaɗa labarai na ƙasar sun rawaito cewar 'yan Taliban sun sace wasu jami'an masu aikin cire nakiyoyi a garin Ghazni da ke a yankin yammaci. Hukumomin tsaro na ƙasar ta Afghanistan sun gargaɗi baƙi da su riƙa sanar da su tafiye-tafiyensu.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Zeinab Mohammed Abubakar