1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sace wani ɗan ƙasar China a Najeriya

Abdourahamane HassaneSeptember 24, 2014

'Yan sanda a Najeriya sun ce wasu 'yan bindiga waɗanda ba a shaida su ba sun sace wani ɗan kasar China a jihar Kogi da ke a yankin tsakiya na ƙasar.

https://p.dw.com/p/1DJoK
29.09.2013 DW online Nigeria Yobe Deu Eng Map Legend

Wani kakakin 'yan sandar na jihar Elvis Aguebor ya shaida wa manema labarai cewar mutumin wanda ma,aikaci ne a ma'aikatar ruwa ta gwamnati,an sace shi tun ranar Talata.

Kuma mutanen da ke ɗauke da makamai sun taras da shi a gidansa idan suka yi awan aba da shi.Tun da farko sai da maharan suka yi harbi cikin iska kafin su tafi da shi.A ranar Lahadin da ta wuce ma, wasu 'yan bindigar sun kai famarki a kan wani ofshin 'yan sanda a jihar.