An sace wata yar jarida a Najeriya
March 23, 2013An ba da rahoton cewar wasu mutane ɗauke da makamai sun yi awun gaba da wata yar jaridar da ke gabatar da shiri a gidan talabijin na gwamnatin ƙasar. Yar jaridar mai suna Olubunmi Oke, wada ke gabatar da shiri a gidan talabijin na NTA, mutanen sun tafi da ita ne bayan saukar ta daga aiki a cikin motarta.
Babban sakataren ƙungiyar yan' jaridu na ƙasar Shu'aibu Usman Leman, ya tabbatar da cewar su na ƙokarin ganin an sako yar jaridar. A ranar Juma'a da ta gabata ma, wasu yan bindigar sun kai hari akan wani gidan kurku da ke a garin Ganye cikin jahar Adamawa, wanda suka fasa gidan yarin. Abin da ya ba da damar tserewar pursunonin, kana daga bisani suka fasa bankuna suka kwashi ganima.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman