1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sace wata yar jarida a Najeriya

March 23, 2013

Wasu ' yan bidiga ne suka sace yar jaridar a garin Akur da ke cikin jihar Ondo a yankin kudu maso yammancin Najeriya.

https://p.dw.com/p/1837f
Schlagworte: Megacities, Lagos, Nigeria, Medien, Zeitungen Wann wurde das Bild gemacht?: 21.12.2009 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Ikoyi, Lagos/Nigeria Bei welcher Gelegenheit/in welcher Situation wurde das Bild aufgenommen? Wer oder was ist auf dem Bild zu sehen?: Medien-Stadt Lagos: Das Angebot an Zeitungen ist vielfältig.
Hoto: DW

An ba da rahoton cewar wasu mutane ɗauke da makamai sun yi awun gaba da wata yar jaridar da ke gabatar da shiri a gidan talabijin na gwamnatin ƙasar. Yar jaridar mai suna Olubunmi Oke, wada ke gabatar da shiri a gidan talabijin na NTA, mutanen sun tafi da ita ne bayan saukar ta daga aiki a cikin motarta.

Babban sakataren ƙungiyar yan' jaridu na ƙasar Shu'aibu Usman Leman, ya tabbatar da cewar su na ƙokarin ganin an sako yar jaridar. A ranar Juma'a da ta gabata ma, wasu yan bindigar sun kai hari akan wani gidan kurku da ke a garin Ganye cikin jahar Adamawa, wanda suka fasa gidan yarin. Abin da ya ba da damar tserewar pursunonin, kana daga bisani suka fasa bankuna suka kwashi ganima.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane

Edita : Usman Shehu Usman