1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An saki Saif al-Islam daga yarin Zintan

Mouhamadou Awal Balarabe
June 11, 2017

Bayan shafe shekaru kusa shida a gidan yarin Zintan bisa zargin ruruta wutar rikicin Libiya, masu tayar da kayar bayan kasar sun saki Saif al-Islam dan marigayi Muammar Gaddafi.

https://p.dw.com/p/2eTA0
Saif al-Islam Gaddafi
Hoto: Reuters/Stringer

Kungiyar masu tayar da kayar baya ta Libiya ta sanar da cewa ta saki Saif al-Islam dan tsohon shugaban Libiya marigayi Muammar Gaddafi daga gidan yarin birnin Zintan bayan yi masa afuwa. Shi da Saif al-Islam da ke zama da na biyu ga marigayin, an zata shi zai gaji mahaifinsa a kan kujerar mulkin Libiya. Amma kuma rikicin da kasar ta yi fama da shi ya sa wata kotu a birnin Tripoli yanke masa hukuncin kisa, amma kuma kungiya masu tayar da kayar baya ta ki mikashi.

Majalisar dokokin kasar Libiya da ke da cibiya a gabashin birnin Tobruk ce ta yi afuwar gama gari da Saif al-Islam Gaddafi ya ci gajiya. Sai dai kotun ICC da ke hukunta manyan laifukan yaki na ci gaba da nemansa ruwa a jallo bisa zargin aikata munanan laifuka lokacin da mahaifinsa Muammar Gaddafi ya yi yunkurin murkushe masu neman sauyi.

A watan Nuwamban 2011 aka kama Saif al-Islam mai shekaru 44 da haihuwa bisa zargin ruruta wutar rikicin kasar Libiya da kuma bada umurnin kashe masu zanga-zangar neman sauyi. Sai dai har yanzu babu wata majiya ta gwamnatin Tripoli da ta tabbatar da sakin nasa.