1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sako wani ɗan ƙasar Jamus da aka sace a Najeriya

Abdourahamane HassaneOctober 30, 2014

An sako mutumin wanda aka sace a makon jiya a Ogun da ke a yanki kudu maso yammacin Najeriya.

https://p.dw.com/p/1Dej6
Baumaschinen der Firma Julius Berger in Abuja Nigeria Archiv 2012
Hoto: picture-alliance/dpa/Michael Kappeler

An ba da rahoton cewar wani ɗan ƙasar Jamus wanda wasu 'yan bindiga suka sace a makon jiya a jihar Ogun a yankin kudu maso yammacin Najeriya an sakoshi.

Kamfanin Julius Berger wanda a nan mutumin yake aiki ya sanar da cewar an sako ma'aikacin nasa salin alin. Sai dai kuma kamfanin mai yin aikin gine-gine a Najeriya bai bayar da arin haske ba a game da yadda aka ako mutumin.