1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An shiga kada kuri'a a zaben kasar Girka

Yusuf BalaJanuary 25, 2015

Neman a yafewa kasar ta Girka kudaden da aka bata bashi na zama abinda ke jan hankulan al'ummar wannan kasa, abin da kuma jam'iyyar Syriza ke cewa na cikin manyan abinda tasa a gaba.

https://p.dw.com/p/1EQ8A
Griechenland Wahlurne 2012
Hoto: Milos Bicanski/Getty Images

Al'ummar kasar Girka sun fita tashoshin kada kuri'a a yau Lahadi,cikin wani muhimmin zabe da aka dade ana jimiransa. Kuri'ar jin ra'ayoyin jama'a dai tun da fari ta nuna cewar jam'iyyar Syriza zata iya samun nasara kan jam'iyyar masu ra'ayin mazan jiya da Firaminista Antonis Samaras.

Jam'iyyar dai ta Syriza ta sha alwashin samar da sauyi ga shirin tallafawa kasar ta Girka dan ta samu ta fita daga matsalar tattalin arziki da kasashen Turai ke yi, inda take son kawo karshen duk wasu sharuda masu tsauri.

A bangaren kasashen da ke bin kasar basuka kuwa na ganin batun yin afuwa ma bai tasoba.