1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An soma taron ƙungiyar ƙasashen G7

Abdourahamane HassaneJune 7, 2015

Shugabannin ƙasashen masu ƙarfin tattalin arzikin masana'antun na yin nazarin batutuwa da dama a Elmau da ke a kudanci Jamus.

https://p.dw.com/p/1Fd0w
G7 Gipfel Schloss Elmau Teilnehmer Gruppenfoto
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Kappeler

Manyan batutuwa da taron ke dubawa sune batun rikicin Ukraine da na matsalar kuɗi da Girka ke fuskanta.Sannan kuma an tsara taron zai taɓo batun kasuwanci da ɗumamayar yanayi da kiwon lafiya da maganar yaƙi da talauci da kuma samar da tsaro.

To sai dai masu fafutuka da ke yin zanga-zanga sun yi yunƙurin datse hanyoyin da ke zuwa zauren taro da ke a Elmau.Abin da ya tilasta wa wasu shugabannin isa wurin ta jiragen sama masu saukar ungulu.