1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An tsagaita wuta a Sudan ta Kudu

May 11, 2014

An fara aiki da yarjejeniyar tsagaita wuta ta Sudan ta Kudu bayan bangorirn da ke rikici da juna sun yi alkawarin yin haka

https://p.dw.com/p/1Bxo2
Hoto: picture-alliance/dpa

Gwamnatin Sudan ta Kudu ta ce an fara aiki da yarjejeyar tsagaita wuta wadda ta kawo karshen yakin basasan kasar na watanni biyar.

Ranar Jumma'a Shugaba Salva Kiir da madugun 'yan tawaye kuma tsohon mataimakin Shugaban kasa Riek Machar suka rantaba hannu kan yarjejeniyar a birnin Addis Ababa na kasar Habasha, yadda ta tanadi tsagaita wuta cikin sa'o'i 24. Kasashen duniya da suka saka kaimi wa bangarorin sun yi maraba da yarjejeyar.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Umaru Aliyu