1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi garkuwa da wani dan Amirka a Nijar

Abdoulaye Mamane Amadou
October 27, 2020

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun tabbatar da sace wani dan Amrika mai aikin mishan a garin Masallata mai nisan kilomita 400 da gabashin birnin Yamai.

https://p.dw.com/p/3kV6K
Niger Agadez Armee Soldaten
Hoto: picture-alliance/Zuma/A. Fox Echols Iii

Da yake magana da manema labarai Ibrahim Abba Lelé kantoman jihar Konni mai makwabtaka da Najeriya, ya ce mutanen da ba a san ko su waye ba sun sace mutumin wanda ya jima a yankin yana rayuwa da iyalinsa a wata gona da ke wajen kauyen na Masallata, sai dai ba a yi wani karin haske kan inda masu garkuwa da shi suka dosa ba.

A cikin watan Oktoban 2016 wasu ‘yan bindiga sun yi sace wani dan Amirka mai aikin jin kai Jeffery Woodke a garin Abalak, daga bisani suka garzaya da shi zuwa kasar Mali, sai dai a shekarar 2019 shugaban kasar Mouhamadou Issoufou ya tabbatar da cewa mutumin na na a raye.

A cikin watan Agustan da ya gabata ma dai kungiyar IS ta dauki alhakin kisan wasu Faransawa shida a wani wurin yawon bude ido na garin Koure mai tazarar kilomita 60 daga birnin Yamai.