1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi harbe-harbe a Hukumar SSS a Najeriya

March 30, 2014

Hukumar tsaro ta farin kaya wato SSS ta bayyana cewar ta shawo kan harbe-harben da manyan bindigogi da aka fuskanta a cibiyarta da ke a Abuja.

https://p.dw.com/p/1BYfM
Polizei in Nigeria
Hoto: Tony Karumba/AFP/Getty Images

Jami'ar yaɗa labarai ta hukumar tsaron ta SSS Merlyn Ogar ta sanar da cewar harbe- harben sun faru ne bayan da wani fursuna ya yi ƙoƙarin karɓe bindigar da ke hannun mai ba shi abinci a ƙoƙarin da ya yi na arcewa daga inda ake tsare das shi.

To sai dai bayanai sun nuna cewar irin ƙarar bindigar da aka riƙa ji na jefa shakku a kan ko yunƙuri ne na arcewar fursunoni a wurin. Malam Aminu Muhammad wani mazauni kusa da unguwar ya bayyana cewar sun kaɗu matuƙa a sakamakon harbe-harben manyan bindigogin.

Mawallafi : Suleiman Babayo
Edita : Abdourahamane Hassane