An yi harbe-harbe a Hukumar SSS a Najeriya
March 30, 2014Talla
Jami'ar yaɗa labarai ta hukumar tsaron ta SSS Merlyn Ogar ta sanar da cewar harbe- harben sun faru ne bayan da wani fursuna ya yi ƙoƙarin karɓe bindigar da ke hannun mai ba shi abinci a ƙoƙarin da ya yi na arcewa daga inda ake tsare das shi.
To sai dai bayanai sun nuna cewar irin ƙarar bindigar da aka riƙa ji na jefa shakku a kan ko yunƙuri ne na arcewar fursunoni a wurin. Malam Aminu Muhammad wani mazauni kusa da unguwar ya bayyana cewar sun kaɗu matuƙa a sakamakon harbe-harben manyan bindigogin.
Mawallafi : Suleiman Babayo
Edita : Abdourahamane Hassane