1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi kakkausar suka kan Koriya ta Arewa

Ahmed Salisu
February 14, 2017

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya yi kakkausar suka ga mahukuntan Koriya ta Arewa bayan da kasar ta yi gwajin wani makami mai linzami a karshen makon da ya gabata.

https://p.dw.com/p/2XXwo
Nordkorea Raketentest U-Boot
Hoto: Reuters/KCNA

Kwamitin har wa yau ya shawarci mambobinsa da su dauki karin matakai wajen tabbatar da cewar takunkumin da aka kakabawa kasar na aiki yadda ya kamata sai dai bai yi karin haske ba kan irin matakan da za a dauka. Wannan dai na zuwa bayan da a jiya Litinin shugaban Amirka Donald Trump wanda kasarsa ke zaman doya da manja da Koriya ta Arewa ya bayyana a wani taron manema labarai cewar Pyongyang matsala ce babba ga duniya wadda a cewarsa za su magance ta amma kuma bai fadi irin hanyoyin da za su bi wajen yin hakan ba.