1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi kira da a kara azama a kan rikicin bashin kasar Girika

Mohammad Nasiru AwalMarch 19, 2015

Shugaban gwamnatin Jamus Angela Merkel ta ce ana bukatar cikakken hadin kai a kokarin warware matsalar bashin.

https://p.dw.com/p/1EtGK
Deutschland Merkel Regierungserklärung vor EU Gipfel
Hoto: Reuters/F. Bensch

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta yi kira ga dukkan bangarorin da rikicin basussukan kasar Girika ya shafa da su kara zage dantse wajen samun maslaha. Merkel ta fada wa majalisar dokokin Bundestag a birnin Berlin cewa ana bukatar hadin guiwa tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki a batun bashin na Girika. Ta yi kashedin cewa idan tsarin takardun kudin bai daya na Euro ya ruguje to nahiyar Turai ma za ta ruguje. A wannan Alhamis shugabannin kasashe da na gwamnatocin kasashen tarayyar Turai za su yi taron kolin yini biyu a birnin Brussels, taron da rikicin kudin kasar Girika ya mamayen ajandarsa. A gefen taron kuma Firaministan Girika Alexis Tsipras zai yi wata haduwa ta musamman da Angela Merkel da shugaban Faransa Francois Holland da kuma manyan wakilan hukumomin kungiyar EU.