1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zargi Iran da keta yarjejeniya

Ahmed Salisu
January 22, 2018

Ministan harkokin wajen Faransa Jean-Yves Le Drian ya bayyana cewar Iran ba ta mutunta wani bangare na yarjejeniya da aka yi kan shirinta na nukiliya wanda a ciki aka haramta mata kera makaman kare dangi.

https://p.dw.com/p/2rKpt
Iran Atomwissenschaftler
Hoto: picture alliance/dpa/epa

Da ya ke jawabi ga manema labarai a birnin Brussels na kasar Beljiyam, Minista Le Drian ya ce shi da takwarorinsu na Kungiyar EU za su yi dukannin mai yiwuwa wajen ganin Iran ta mutunta yarjejeniya da aka yi da ita. Baya ga wannan, ministan ya ce za su sake jaddadawa Iran din rashin jin dadinsu game da irin katsalandan da ta ke yi a kasashen Yemen da Lebanon da Siriya wanda a cewarsa na jawo rarrabuwar kai. Ya zuwa yanzu dai Iran ba ta kai ga maida martani kan kalaman na Le Drian ba.