1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zargi sojin AMISOM da fyade a Somalia

September 8, 2014

Hukumar kare hakkin dan adam ta Human Rights Watch ta zargi rundunar kiyaye zaman lafiya ta AMISOM da yiwa mata da dama ciki kuwa har da 'yan shekaru 12 fyade a Somalia.

https://p.dw.com/p/1D8oz
AU Soldat in Modagischu
Sojin rundunar AMISOM dubu ashirin da biyu daga kasashen Afirka shidda ne ke aiki a SomaliaHoto: picture-alliance/dpa

A wani rahoto da Human Rights Watch din ta fidda ta ce wasu daga cikin matan da aka yi wa fyaden sun ce sojin sun basu abinci da 'yan kudade domin nuna cewa kamar da amincewarsu suka yi amfani da su.

To sai dai rudunar sojin ta AMISOM ta bakin kwamadanta Janar Silas Ntigurirwa ta musanta wannan zargi da ake wa dakarunta inda ya ce rahoton da Human Rights Watch ta fidda bai yi musu adalci ba kuma ya na cike da gibi matuka.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammad Nasiru Awal