1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci gaba da tura dakaru domin kawar da 'yan tawayen Mali

January 18, 2013

Kungiyar Tarayyar Turai ta amince da tura daruruwan dakaru domin taimakawa wajen haros da dakarun sojan kasar Mali

https://p.dw.com/p/17Mg5
Nigerian Army soldiers stand as part of preparations for deployment to Mali, at the Nigerian Army peacekeeping centre in Jaji, near Kaduna January 17, 2013. French troops launched their first ground assault against Islamist rebels in Mali on Wednesday in a broadening of their operation against battle-hardened al Qaeda-linked fighters who have resisted six days of air strikes. West African military chiefs said the French would soon be supported by around 2,000 troops from Nigeria, Chad, Niger and other regional powers - part a U.N.-mandated deployment which had been expected to start in September but was kick-started by the French intervention. REUTERS/Afolabi Sotunde (NIGERIA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST MILITARY)
Hoto: Reuters

Kungiyar Tarayyar Turai ta amince da tura daruruwan dakaru domin taimakawa wajen haros da dakarun sojan kasar Mali, karkashin jagorancin Janar Leh-Quantre na kasar Faransa, wanda zai jagoranci aikin na horas da sojojin.

Cikin watan gobe na Febrairu ake fara cikekken aikin, amma cikin kwanaki masu zuwa ake saran tawogar farko ta masu bada taimakon kayan aiki za ta isa Bamako babban birnin kasar ta Mali. Ministan harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle ya tabbatar da haka cikin sanarwar da aka fitar.

Ana ci gaba da kai dauki ga kasar ta Mali, inda dakarun Faransa da su ka kaddamar da samame ke ci gaba da sasakan 'yan tawaye, kuma su na samun tallafi daga kasashen Afirka da ke ci gaba da tura sojoji. Sojojin Najeriya, Togo da Chadi na cikin wadanda ke ci gaba da isa, kuma bisa yadda aka tsara dakarun Afirka za su yi aikin karkashin Komandan sojan da Najeriya ta nada. Yayin da Faransa ke kara yawan dakaru da ci gaba da mamaye yankunan kasar ta Mali domin dakile karfin 'yan tawayen da mayar da yankuna karkashin ikon gwamnati.

Mawallafi: Suleiman Babayo

Edita: Halima Balaraba Abbas