1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana zaben 'yan majalisar dokoki na Turkiya

Suleiman BabayoNovember 1, 2015

Zaben majalisar dokokin kasar ta Turkiya zai tantance inda gwamnatin za ta fuskanta.

https://p.dw.com/p/1Gxtu
Türkei Wahlen Wahllokal Wählerin Stimmabgabe
Hoto: Reuters/U. Bektas

Ana ci gaba da kada kuri'a a zabe kasa baki daya da ke wakana a kasar Turkiya, inda jam'iyya mai mulki ta AKP take fata kan samun kujerun majalisar dokoki da take bukata domin samun damar kafa gwamnati kai tsaye.

A zaben watan Yuni, kimanin watanni biyar da suka gabata, jam'iyyar Shugaba Recep Tayyip Erdogan mai mulki ta rasa rinjayen da take bukata a karo na farko cikin shekaru 13, abin da ya haifar da rashin iya kafa gwamnati, da ya janyo sake kiran zabe karo na biyu a shekara guda, a kasar mai mutane kimanin milyan 80. An jibge dubban jami'an tsaron musamman cikin yankunan Kurdawa na kasar ta Turkiya, saboda tabbatar da doka da oda.