Ana farautar wasu ma'aikata 100 a Turkiya
August 2, 2016Talla
Gwamnatin kasar Turkiya ta sake bada umarnin kame wasu ma'aikata 100 ciki har da wasu manyan likitoci a asibitin sojoji da ke birnin Ankara. Jami'an gwamnatin kasar sun bayyana wannan yunkuri a matsayin bude sabon babin bincike a kan yunkurin kifar da gwamnatin Recep Tayyib Erdogan da bai cimma nasara ba a watan da ya gabata.
Ana dai zargin wasu ma'aikatan asibitin da bai wa 'yan kungiyar Fethulla Gulen bayanan sirri, wannan ya sa gwamnatin ke daura alhakkin yunkurin juyin mulkin a kan kungiyar ta Fethulla Gulen.
Gwamnatin Erdoan ta kori dubban ma'aikata a matakai daban-daban ciki har da na soje tun bayan yunkurin juyin mulki.