1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana farautar wasu ma'aikata 100 a Turkiya

Abdul-raheem HassanAugust 2, 2016

Ana zargin wasu jami'an asibitin sojoji da hannu a yunkurin kifar da gwamnatin shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan.

https://p.dw.com/p/1JaNT
Türkei - Erdogan besucht Police Special Operation Department's Headquarters
Hoto: picture-alliance/AA/K. Ozer

Gwamnatin kasar Turkiya ta sake bada umarnin kame wasu ma'aikata 100 ciki har da wasu manyan likitoci a asibitin sojoji da ke birnin Ankara. Jami'an gwamnatin kasar sun bayyana wannan yunkuri a matsayin bude sabon babin bincike a kan yunkurin kifar da gwamnatin Recep Tayyib Erdogan da bai cimma nasara ba a watan da ya gabata.

Ana dai zargin wasu ma'aikatan asibitin da bai wa 'yan kungiyar Fethulla Gulen bayanan sirri, wannan ya sa gwamnatin ke daura alhakkin yunkurin juyin mulkin a kan kungiyar ta Fethulla Gulen.

Gwamnatin Erdoan ta kori dubban ma'aikata a matakai daban-daban ciki har da na soje tun bayan yunkurin juyin mulki.