1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana gudanar da bincike a Amirka

September 17, 2013

Bayan harin da wani tsohon jaim'in sojin ruwa na ƙasar ya kai a kan ginin cibiyar sojojin ruwan a Washington wanda a ciki ya harbe mutane 12, kafin a kashe shi.

https://p.dw.com/p/19jEn
A combination photo shows Aaron Alexis, who the FBI believe to be responsible for the shootings at the Washington Navy Yard in the Southeast area of Washington, DC, is shown in this handout photo released by the FBI on September 16, 2013. The 34-year-old gunman opened fire at the U.S. Navy Yard in Washington on Monday in a shooting that left 13 people dead at the busy military installation not far from the U.S. Capitol and the White House, officials said. Alexis of Fort Worth, Texas, was among the dead and authorities said they were searching for another possible gunman wearing military-style clothing. REUTERS/FBI/Handout via Reuters (UNITED STATES - Tags: HEADSHOT CRIME LAW) FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS-- eingestellt von haz
Hoto: Reuters

Jami'an tsaron Amirka sun ce sun fara gudanar da bincike da ma dai tattara sakamako dangane da dalilan harin da wani ɗan bindigar ya kai wa wani ginin sojin ruwan ƙasar a jiya Litinin wanda ya yi sanadiyyar rasuwar mutane sha uku ciki har da ɗan bindigar, baya ga wasu da dama da suka jikkata.

Tuni dai jami'an tsaro na FBI suka bayyana sunan Aaron Alexis wanda a baya jami'i ne na sojin ruwan ƙasar a matsayin wanda ke da hannu wajen hari har ma abokansa sun fara ba da ba'asi dangane da hallayyarsa inda wasu ke cewar kamili ne, sai dai sun ce akwai wata jiƙaƙƙiya tsakaninsa da rundunar sojin ruwan ƙasar.

Gwamnatin AmIrka ta nuna damuwarta dangane da wannan hari inda shugaba Barack Obama ya ba da ummarnin sassauto da tutocin ƙasar ƙasa-ƙasa har ranar Jumma'a don yin alhinin waɗanda suka rasu a ƙoƙarinsu na kare al'ummar ƙasar.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mohamadou Awal Balarabe