1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mahara sun kashe mutane a Katsina

Zainab Mohammed Abubakar
June 13, 2020

Wasu 'yan bindiga sun halaka rayukan mutane a kananan hukumomi biyu na jihar Katsina ciki har da mai garin Faru, Dikko Usman, da ke karamar hukumar Matazu.

https://p.dw.com/p/3dj0m
Symbolbild | Nigeria | SWAT
Hoto: AFP/Y. Chiba

Haka kuma maharan sun kashe wasu mutane a garin 'Yan kara da ke karamar Hukumar Faskari duk dai a jihar ta Katsina.

Lamarin ya faru ne a daren jiya Juma'a inda maharan suka kai hare-haren ta hanyar budewa mutane wuta.

Yunkurin wakilinmu Yusuf Ibrahim Jargaba na tuntubar kakakin rundunar 'yan sadan jihar Katsina SP Isa Gambo ya ci tura, saboda bai amsa wayarsa ba.

Karuwar hare-haren na zuwa ne a daidai lokacin da mahukuntan Najeriyar ke ikirarin aniyar murkushe 'yan bindigar.