1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

AU ta yi Allah Wadai da harin Somaliya

Kamaluddeen SaniFebruary 29, 2016

Babban jami'in Tarayyar Afrika a Somaliya Francisco Caetano Madeira ya soki mummunan harin da kungiyar al-Shabbab ta kai a birnin Baidoa a ranar lahadin nan.

https://p.dw.com/p/1I4Ft
Somalia Anschlag Explosion in Baidoa
Hoto: Getty Images/AFP

Birnin dai na Baidoa wanda ke samun kulawar dakarun hadaka na rundunar Tarayyar Afrika kimanin dubu 22 mai suna AMISOM ya fuskani harin kungiyar ta al-Shabbab ne a ranar lahadi nan. A inda mutane kimamin 30 suka hallaka a yayin da wasu 61 suka samu raunuka daban-daban.

A nasa bangaren gwamnan birnin Abdurashid Abdullahi ya ce, daga cikin wadanda suka sami raunuka, 15 suna nan cikin mawuyacin hali a inda ya kara da cewar harin ya faru akan cikin tsakiyar wani wajen hada-hadar harkoki ciki da mutane a birnin na Baidoa.

Tuni dai kungiyar ta Al-shabbab ta yi ikirarin cewar itace ke da alhakin harin na Somaliya.