1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ba za a yi zabe bana a Jamhuriyar Kongo ba

July 10, 2017

Hukumar zabe a Jamhuriyar demokradiyyar Kongo ta ce ba za'a iya gudanar da zaben shugaban kasa dana yan majalisun dokoki a kasar kafin karshen wannan shekarar ba.

https://p.dw.com/p/2gIYZ
Joseph Kabila Präsident Demokratische Republik Kongo
Hoto: Getty Images/AFP/T. Mianken

Shugaban hukumar zaben Corneille Nangaa ya shaidawa manema labarai a Kinshasa babban birnin kasar cewa zai yi matukar wuya a iya gudanar da zaben kafin watan Disamba.

A karshen wannan shekarar ce dai ya kamata a gudanar da zaben bisa yarjejeniyar da aka cimma domin kaucewa tashin hankali bayan da shugaban kasar Joseph Kabila da ya dade a karagar mulki yaki amincewa ya sauka a karshen wa'adin mulkinsa a watan Disambar bara.

Jami'yyun adawa sun soki lamirin matakin da cewa tamkar wata takalar fada ce da kuma daure wa gwamnatin gindin cigaba da zama a karagar mulki.