1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Babban zabe a Mozambik

October 15, 2014

Masu kada kuri'a a babban zaben kasar Mozambik sun yi dandazo zuwa rumfunan zabe, domin kada kuri'unsu a zabukan shugaban kasa da na 'yan majalisar dattawa.

https://p.dw.com/p/1DW2s
Hoto: Getty Images/AFP/Gianluigi Guercia

Wannan dai na zuwa ne watanni kalilan bayan da bangarorin siyasar kasar biyu wato Frelimo da Renamo da ke gaba da juna na tsahon shekaru biyu suka cimma yarjejeniyar sulhu a tsakaninsu. Bayan da ya kada kuri'arsa a Maputo babban birnin kasar, shugaban jami'iyyar adawa ta Renamo Afonso Dhlakama ya bayyana cewa ya na da tabbacin zaben zai gudana cikin gaskiya da adalci . Shima dai Filipe Nyusi dantakarar jam'iyya mai mulki ta Frelimo ya kada kuria'ar ta sa ne a birnin na Moputu, yayin da dantakarar sabuwar jam'iyyar "Mozambique Democracy Movement" Daviz Simango ya kada kuri'arsa a birnin Beira da ke zaman birni na biyu mafi girma a kasar ta Mozambik.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Umaru Aliyu