1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Babu alamun warware rikicin Mali a nan kusa

January 22, 2013

Rundunar sojin Mali ta ce zai dauki kimanin wata guda kafin samun gagarumar nasara akan 'yan tawayen kasar.

https://p.dw.com/p/17PuJ
GettyImages 159820372 Malian soldiers sit at the back of a pickup truck as they arrive in the city of Diabaly on January 21, 2013. French and Malian troops today recaptured the Malian towns of Diabaly and Douentza from Islamist fighters, France's defence minister said.French and Malian troops earlier today entered Diabaly, which has been the theatre of air strikes and fighting since being seized by Islamists a week ago, an AFP journalist witnessed. AFP PHOTO / ISSOUF SANOGO (Photo credit should read ISSOUF SANOGO/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

Hafsan sojin Mali ya fadi a wannan Talatar (22.01.2013) cewar, dakarunsa da ke samun goyon bayan sojin Faransa za su dauki tsawon wata guda suna fafatawa gabannin kwace iko da biranen Gao da kuma Timbuktu daga hannun 'yan tawayen Mali.

Hafsan sojin ya fadi hakanne a dai dai lokacinda wasu jiragen saman Amirka suka fara jigilar karin dakarun Faransa zuwa kasar ta Mali, kana wani jami'in ma'aikatar tsaron Malin daya bukaci a sakaya sunansa ya ce sojojin Faransa sun yi ruwan bama-bamai akan sansanin mayakan 'yan tawayen da ke da ala'ka da kungiyar alQa'ida kusa da birnin na Timbuktu, mai dadadden tarihi.

Tunda farko dai kakakin ma'aikatar kula da harkokin tsaron Mali, Thierry Burkhard ya bayar da tabbacin cewar dakarun sun jefa bama-bamai a wajen birnin na Timbuktu.

Kasashen duniya na matsa kaimi wajen tallafawa Faransa da sauran dakarun kasashen yankin yammacin Afirka a gangamin da suka kaddamar na fatattakar 'yan tawayen Mali, wadanda suka yi tsawon watanni tara suna rike da iko a yankunan arewacin kasar.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe