1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Barack Obama ya yi kiran tattaunawa da Iran

Abdorahamane HassaneMarch 20, 2015

Shugaban na Amirka ya yi kira ga hukumomin na Iran da su ba da haɗin kai ga ci gaban tattauna shirin nukiliya na ƙasar.

https://p.dw.com/p/1EuKO
USA Selma 50. Jahrestag Blutiger Sonntag von 1965 Präsident Obama
Hoto: Reuters/Jonathan Ernst

Shugaba Barack Obama ya gargaɗi shugabannin ƙasar ta Iran da su yi amfani da damar da ake da ita mai cikke da tarihi domin ganin an cimma matsaya ɗaya a kan shirin nukiliya na ƙasar

Obaman dai ya ce kwanaki na gaba masu zuwa za su kasance masu mahimmanci, kana kuma ya ce an samu ci gaba wajen tattaunawa sai dai har yanzu ya ce akwai saɓanni da ke tsakaninsu da ƙasar ta Iran a kan batun.