1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Batun tsaro na barazana ga hadin kan Najeriya

October 29, 2012

Hare- haren ta’addanci a Najeriya na kara haifar da damuwa game da makomar kasar da na al'umarta. Ko wace illa hakan ke da shi ga hadin kan kasa musamman kwan gaba kwan baya da wannan matsala ke yi?

https://p.dw.com/p/16ZAU
Hoto: picture-alliance/dpa

A shekarun baya dai ba a san hare-hare na ta'adanci da kunar bakin wake ba a Najeriya. Amma a yanzu suna ci gaba da zama ruwan dare duk da matakan tsaro da gwamnati ta dade tana ikirarin dauka a kansu. Tuni dai Kokarin tabbatar da tsaron ya haifar da tsoro a zukattun 'yan Najeriyar da ke cike da fargabar wannan matsala.

Salon irin na dauki dai dai da ake yi wa jama'a da kuma jami'an tsaron kasar na kara zama babbar barazana ga harkokin tsaro. Masharhanta sun bayyana ta da wacce kasar bata taba fuskantar irinta ba tun bayan samun 'yancin kai shekaru 52 da suka gabata, duk kuwa da fafata yaki da ta yi a 1967 zuwa 1970. Major Yahya Shunku mai ritaya kwararre ne a harkar tsaron Najeriyar ya ce‘ " Alhakin yan sandan ciki ne su tabbatar da cewa duk wani abu da zai ta da hankalin kasa sun shawo kansa kaman irin tashin bama-baman nan. To amma daga lokacin da aka fara samun tashin bama –baman nan babu wani darakta na hukumar SSS na wata jiha da aka kama da sakaci a aikinsa, duk wanda ake kamawa sai dai ka ji an ce 'yan sanda."

epa03046192 (FILE) A file photograph Nigerian president Goodluck Jonathan (2-L) standing on the back of a vehicle as he is driven after he was sworn in as president during a ceremony in Abuja, Nigeria 29 May 2011. Media reports state on 31 December 2011 that President Goodluck Jonathan has declared a state of emergency in areas affected by attacks from the Islamist group Boko Haram. Borders will be temporarily closed in the north-eastern states of Yobe and Borno, and central state of Plateau. EPA/STR *** Local Caption *** 00000402757844
Shugaba Jonthan ya ce ya na daukan matakaiHoto: picture-alliance/dpa

Wadanda ke da alhakin tabbatar da tsaro a Najeriya

Irin kwan gaba kwan bayan da wannan matsala ta ta'adanci ke ci gaba da yi a Najeriya ya sa ta zama kadangaren bakin tulu. Sai dai makudan kudin da aka kasaftawa sashin tsaro da bana suka zartar Naira triliyan guda. Lamarin ya sanya nuna damuwa bisa ga barazanar da matsalar ta'adanci ke yi ga hadin kan Najeriyar da a yanzu ke fuskantar sabon kalubale na bangaranci. Abinda ya sanya Dr Abubakar Umar Kari masanin hallayar jama'a da ke jami'ar Abuja bayyana tsoron cewa " Abubuwa sun tabarbare matuka da ke nuna komai na iya faruwa, tun da abubuwan da ke faruwa a yanzu wadanda sabbi ne ba a Arewa ba a ma Najeriya baki daya. Sai dai kawai a zo ayi ta Magana ta fatar baki ana cewa yau za'a dau wannan mataki, gobe a yi ikirarin wancan, amma babu matakin da ake dauka, a yanzu dai babu ban san ko a nana gaba ba.''

This image taken from video posted by Boko Haram sympathizers shows the leader of the radical Islamist sect Imam Abubakar Shekau made available Wednesday Jan. 10, 2012. The video of Imam Abubakar Shekau cements his leadership in the sect known as Boko Haram. Analysts and diplomats say the sect has fractured over time, with a splinter group responsible for the majority of the assassinations and bombings carried out in its name. (AP Photo) THE ASSOCIATED PRESS CANNOT INDEPENDENTLY VERIFY THE CONTENT, DATE, LOCATION OR AUTHENTICITY OF THIS MATERIAL
Ba a san inda shugaban Bokoram Shekau ya ke baHoto: AP

Mafita ga matsalar tsaro da ake fuskanta a Najeriya

Tuni wasu ke hangen wauta ce a tekun maganinki Allah ya sanya ci gaba da laluben mafita. Kwararru sun dade da nanata bukatar sulhu. Amma ga Malam Bashir Baba da ke zama mai sharhi a kan al'ammuran hanya daya ce ta sauki. "Ana iya samun sauki idan mahukunta wadanda amanar jama'a take hannunsu suka fitar da son zuciya. To ana iya samun sauki amma daina wannan al'ammari gaskiya ni ba ganshi ba."

Anobar da wannan matsala ta rashin tsaro da Najeriya ke fiskanta, na zama abu mai ta da hankali ga makomar kasar da a lokutan baya ke zama abin misalai wajen zaman lafiya da kwanciya hankali.

Mawallafi: Uwais Abubakar Idris
Edita: Mouhamadou Awal