1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bauchi: Fada ya kaure tsakanin jami'an tsaro da 'yan siyasa

Abdourahamane Hassane
March 10, 2019

Fada ya barke tsakanin jami'an tsaro da wasu wakilan jam'iyyun siyasa a cibiyar hukumar zabe ta INEC a Jihar Bauchi inda jami'an tsaron suka lakkada musu duka. 

https://p.dw.com/p/3Ekrt
Nigeria Abuja Proteste von Schiiten des Islamic Movement
Hoto: Getty Images/AFP/S. Heunis

Rikicin ya taso ne sakamakon gaza bayyana sakamakon zaben karamar hukumar Tafawa Balewa da shugabar zaben jihar ta gaza yi a karo na biyu. Wannan lamari shi ya haddasa wakilan jam'iyyun suka nuna rashin amincewa da matakin da suke ganin akwai rufa-rufa a ciki.