1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A farkon badi za a gudanar da taron tallafa wa Siriya

Mohammad Nasiru AwalNovember 16, 2015

A shekara mai kamawa ta 2016 gwamnatocin Birtaniya da Jamus za su shirya babban taron tara kudaden tallafa wa Siriya mai fama da yakin basasa.

https://p.dw.com/p/1H6n1
Syrien-Konferenz in Wien
Hoto: Reuters/L. Foeger

Shugabannin kasar Birtaniya da Jamus sun ce za su gudanar da wani taro a farkon shekara mai zuwa don tara kudin tallafi ga 'yan Siriya da yakin kasar ya daidaita, wadanda kuma ke cikin halin kuncin rayuwa. A lokacin da suke magana a gefen taron kungiyar kasashe masu tagomashin tattalin arziki na G-20 a kasar Turkiyya, kasashen Jamus da Birtaniya sun ce tallafin da ake samu daga kasashen duniya ya ragu matuka. Yakin basasar Siriya ya haddasa matsalar 'yan gudun hijira mafi muni a Turai tun bayan yakin duniya na biyu. Miliyoyin 'yan kasar sun rasa muhallansu yayin da kimanin dubu 250 suka mutu a yakin tsakanin dakarun gwamnati da na kungiyoyin 'yan tawaye ciki har da kungiyar IS mai da'awar kafa daular Musulunci a Iraki da Siriya.