1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar Boko Haram ta sake kai hari

Lateefa Mustapha Ja'AfarMay 15, 2015

Wasu da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram da ke gwagwarmaya da makamai a Tarayyar Najeriya sun kai wani hari a wajen garin Maiduguri babban birnin jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin kasar.

https://p.dw.com/p/1FQSx
Nigeria Armee rettet Mädchen Symbolbild
Hoto: picture-alliance/dpa/H. Ikechukwu

Rahotanni sun nunar da cewa maharan sun kai farmaki da misalin karfe uku na wannan Jumma'a a agogon Najeriya karfe biyu ke nan agogon GMT. Harin wanda aka kai a wajen birnin na Maiduguri a wani guri da aka sake tsugunar da mutanen da rikicin kungiyar ta Boko Haram ya tarwatsa da ke da nisan misalin kilomita 10 da garin na Maiduguri.

Kawo yanzu ba a tabbatar da adadin wadanda suka mutu ko kuma suka jikata a wannan harin ba wanda ke zaman na biyu cikin wannan makon da 'yan kungiyar ta Boko Haram suka kai a Maidugurin fadar gwamnatin jihar Borno.